

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jajantawa gwamnati da al’ummar kasar Kenya bisa rasuwar shugaban ‘yan adawar kasar na farko Mwai Kibaki.
Shugaba Buhari, a wata sanarwa da ya fitar jiya ta hannun mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Garba Shehu, ya ce, Marigayi Kibaki ya kafa tarihin zama dan siyasa na farko da ya kawo karshen mulkin jam’iyya daya, bayan ta shafe shekaru 40 tana mulki a kasar, ya kuma kawo karshen ta a shekarar 2013.
Ya kuma ce Kibaki ya nuna cewa, dayin hakuri da juriya ne kadai, mutum zai iya cimma burinsa na rayuwa.
Garba Shehu ya ci gaba da cewa, mafi akasarin mutane suna barin gwagwarmaya ne bayan wasu ‘yan shekaru kadan, amma Kibaki ya tsaya kyam, ya kawo karshen mulkin jam’iyya daya data shafe shekaru 40 tana mulki a kasar.