Shugaba Buhari ya umarci hukunta wadanda suka shigo da gurbataccen mai cikin Najeriya

0 94

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a jiya ya umarci hukunta wadanda suka shigo da gurbataccen mai cikin kasarnan.

Gwamnatin Tarayya a ranar Talata tace sinadarin methanol da aka samu kwanannan a cikin man fetur din da aka shigo da shi, ya wuce kima.

Lamarin ya jawo karancin man da dogayen layukan ababen hawa a gidajen man manyan birane irinsu Lagos da Abuja.

Gwamnati a ranar Laraba tace an samu karancin mai na kwanaki 10 a guraren adana man fetur na kasa.

A ranar Larabar, gwamnatin tarayya tace zata gudanar da gagarumin bincike domin sanin yadda aka shigo da gurbataccen man fetur cikin kasarnan.

A wata sanarwa da aka fitar a ranar ta laraba da yamma, managing daraktan kamfanin mai na kasa NNPC, Mele Kyari ya lissafa kamfanin MRS da Oando da sauransu a matsayin wadanda suka shigo da gurbataccen man.

Leave a Reply

%d bloggers like this: