

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Fadar shugaban kasa ta ce a yau ne shugaban kasa Muhammadu Buhari zai fara wata ziyarar kwanaki hudu zuwa birnin Addis Ababa babban birnin a kasar Habasha.
Buhari Zai halarci zaman taron shugabannin kasashen Afirka karo na 35.
Mai magana da yawun shugaban kasar, Femi Adesina ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar jiya a Abuja.
Femi Adesina ya ce shugaba Buhari zai bi sahun sauran shugabannin Afirka wajen nemo hanyoyin magance kalubalen siyasa, tattalin arziki da zamantakewar nahiyar.
Ya ce, Shugaba Buhari zai gana da wasu shugabannin kasashe domin inganta huldar kasuwanci, da hada kai don tinkarar kalubalen tsaro da kuma kulla alaka a bangarori daban-daban domin samun ci gaba mai dorewa.
Femi Adesina ya ce shugaban zai samu rakiyar Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama, Ministan Lafiya, Osagie Ehanire, Ministan Noma, Mohammed Abubakar da Ministan Harkokin Agaji, Kula da Annoba da Walwalar Jama’a, Sadiya Umar Farouk.