

- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Mai bawa shugaban kasa shawara akan kafafen yada labarai, Femi Adesina, yace shugaban kasa Muhammadu Buhari zai sanya hannu akan kudirin dokar zabe da aka yiwa gyara.
Femi Adesina ya sanar da haka a yau lokacin da ake fira da shi a gidan talabijin na Channels.
Kakakin na shugaban kasa lokacin da yake kare ubangidansa, ya soki wadanda ke zargin shugaba buhari da jinkiri wajen sanya hannu akan kudirin.
Yace jinkirin na shugaban kasa har yanzu yana bisa turbar tanade-tanaden kundin tsarin mulki.
Tunda farko shugaban kasar, ya ki amincewa ya sanya hannu akan kudirin dokar zaben na shekarar 2021 da aka aika masa a ranar 19 ga watan Nuwamban bara, domin bawa jam’iyyun siyasa damar zaben ‘yan takar-karun zabe ta hanyoyi daban-daban.
Majalisun kasa sun gyara hakan kuma sun sake aikawa shugaban kasa kudirin dokar domin ya sanya hannu.