Tattaunawa Da Barayi Ce Mafitar Matsalar Tsaro – Matawalle

0 128

Gwamna Bello Matawalle na jihar Zamfara yace tattaunawa da barayi ‘yan bindiga ita ce hanya mafi dacewa wajen dorewar zaman lafiya a jihar, inda yace baya dana sanin kasancewar gwamnatinsa ta bi wannan hanyar.

Matawalle ya fadi haka daidai lokacin da ake ta tofa albarkacin bakuna akan ingancin hanyoyin da ake bi wajen magance matsalar tsaro da ta ki ci, ta ki cinyewa a Arewa maso Yamma.

Yace duk da tarin sojojin da aka kawo da kuma luguden wutar da ake ta yiwa barayi babu kakkautawa, karkashin gwamnatinsa, kashe-kashen barayi yan bindiga na cigaba da karuwa a wani lamari mai firgitarwa.

Leave a Reply

%d bloggers like this: