Gwamna Bello Matawalle na jihar Zamfara yace tattaunawa da barayi ‘yan bindiga ita ce hanya mafi dacewa wajen dorewar zaman lafiya a jihar, inda yace baya dana sanin kasancewar gwamnatinsa ta bi wannan hanyar.
Matawalle ya fadi haka daidai lokacin da ake ta tofa albarkacin bakuna akan ingancin hanyoyin da ake bi wajen magance matsalar tsaro da ta ki ci, ta ki cinyewa a Arewa maso Yamma.
- Amurka ta ce jami’anta na ganawa da sojojin da ke mulki a Jamhuriyar Nijar
- Gwamnatin jihar Jigawa ta fito da wani shiri na amfani da fasaha wajen koyo da koyarwa a jihar
- Kungiyar NULGE reshen karamar Hukumar Buji ta yabawa wakilin mazabar Buji a majalisar dokoki
- Aƙalla fursunoni 118 ne suka tsere daga gidan yarin Suleja
- Kasashen Afirka sun amince su yi magana da murya daya domin yaki da ta’addanci
Yace duk da tarin sojojin da aka kawo da kuma luguden wutar da ake ta yiwa barayi babu kakkautawa, karkashin gwamnatinsa, kashe-kashen barayi yan bindiga na cigaba da karuwa a wani lamari mai firgitarwa.