Gwamna Bello Matawalle na jihar Zamfara yace tattaunawa da barayi ‘yan bindiga ita ce hanya mafi dacewa wajen dorewar zaman lafiya a jihar, inda yace baya dana sanin kasancewar gwamnatinsa ta bi wannan hanyar.
Matawalle ya fadi haka daidai lokacin da ake ta tofa albarkacin bakuna akan ingancin hanyoyin da ake bi wajen magance matsalar tsaro da ta ki ci, ta ki cinyewa a Arewa maso Yamma.
- Ina alfahari da samun dimbin goyon bayan da ake bukata domin zama ‘yartakara – Kamala Harris
- An bukaci mazauna jihar Jigawa da su kula da matakan kariya domin dakile ambaliyar ruwa
- Ƙasashe 58 sun goyi bayan Ngozi Okonjo-Iweala ta yi tazarce a Shugabar Kungiyar Cinikayya ta Duniya
- Kungiyar Kwadago ta yi gargadi kan yunkurin dakushe zanga-zangar da ake shirin yi a fadin kasar
- Gwamnatin Tarayya ta gabatar da buƙatar ƙarin Naira tiriliyan 6.2 akan kasafin kuɗin bana
Yace duk da tarin sojojin da aka kawo da kuma luguden wutar da ake ta yiwa barayi babu kakkautawa, karkashin gwamnatinsa, kashe-kashen barayi yan bindiga na cigaba da karuwa a wani lamari mai firgitarwa.