Akalla mutane 21 ake fargabar sun mutu bayan wani jirgin ruwa ya kife cikin kogin Benue a Makurdi, babban birnin jihar Benue, jiya da rana.
A cewar wata majiya wacce ta shaida lamarin da idonta, wadanda hatsarin ya rutsa da su mambobin wata coci ce a garin Ijaha dake yankin karamar hukumar Makurdi, wadanda ke kan hanyarsu ta zuwa wani taro a tsallaken kogin.
- IFFHS Ta Saɓa da FIFA, Ta Ayyana Lionel Messi A Matsayin Gwarzon Ɗan Wasan Gasar Kofin Duniya
- Casemiro Ya Koma Inter Miami Kyauta Bayan Karewar Kwantiraginsa
- Hisbah Ta Gargadi Masu Neman Shiga Shirin Auren Gata Kan Masu Damfara
- Trump Ya Aike Wa Tinubu Wasiƙa, Ya Yaba da Ƙwazon Gwamnatinsa Wajen Yaƙi da Ta’addanci
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
Kakakin rundunar yansanda na jihar, DSP Catherine Anene, wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin cikin wata sanarwa a madadin kwamishinan yansanda, Mukaddas Garba, yace an kaiwa yansanda rahoton aukuwar hatsarin a jiya da misalin karfe 2 da rabi na rana.