Akalla mutane 21 ake fargabar sun mutu bayan wani jirgin ruwa ya kife cikin kogin Benue a Makurdi, babban birnin jihar Benue, jiya da rana.
A cewar wata majiya wacce ta shaida lamarin da idonta, wadanda hatsarin ya rutsa da su mambobin wata coci ce a garin Ijaha dake yankin karamar hukumar Makurdi, wadanda ke kan hanyarsu ta zuwa wani taro a tsallaken kogin.
- Al’ummar Indiya sun fara kaɗa kuri’a a zaɓen da aka kasa gida bakwai cikin makonni shida
- Jami’an ‘yan sanda a Katsina sun dakile wani hari da aka kai garin Sabuwa dake jihar
- Rundunar sojin Najeriya ba za ta tsagaita ba wajen kawar da masu aikata miyagun laifuka
- Shugaba Bola Tinubu ya amince da wasu tsare-tsare guda uku don inganta fannin ilimi a kasar nan
- Gwamnatin jihar Nasarawa ta dakatar da duk wata Ƙungiyar ’yan banga a jihar
Kakakin rundunar yansanda na jihar, DSP Catherine Anene, wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin cikin wata sanarwa a madadin kwamishinan yansanda, Mukaddas Garba, yace an kaiwa yansanda rahoton aukuwar hatsarin a jiya da misalin karfe 2 da rabi na rana.