

Akalla mutane 21 ake fargabar sun mutu bayan wani jirgin ruwa ya kife cikin kogin Benue a Makurdi, babban birnin jihar Benue, jiya da rana.
A cewar wata majiya wacce ta shaida lamarin da idonta, wadanda hatsarin ya rutsa da su mambobin wata coci ce a garin Ijaha dake yankin karamar hukumar Makurdi, wadanda ke kan hanyarsu ta zuwa wani taro a tsallaken kogin.
- Kuji tsoron Allah ko koma gare Shi, Atiku yayi kira ga yan Najeriya.
- Goodluck Jonathan: Kuri’un talakawa ya kamata su tattance zabe ba kotu ba
- Sarkin musulmi: Gobe Talata shine daya ga watan Ramadan
- Kamfanin Twitter zai kafa reshe a Afirka
- Kungiyar Barcelona ta fi ko wacce kungiya kudi a duniya
Kakakin rundunar yansanda na jihar, DSP Catherine Anene, wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin cikin wata sanarwa a madadin kwamishinan yansanda, Mukaddas Garba, yace an kaiwa yansanda rahoton aukuwar hatsarin a jiya da misalin karfe 2 da rabi na rana.