Akalla mutane 21 ake fargabar sun mutu bayan wani jirgin ruwa ya kife cikin kogin Benue a Makurdi, babban birnin jihar Benue, jiya da rana.
A cewar wata majiya wacce ta shaida lamarin da idonta, wadanda hatsarin ya rutsa da su mambobin wata coci ce a garin Ijaha dake yankin karamar hukumar Makurdi, wadanda ke kan hanyarsu ta zuwa wani taro a tsallaken kogin.
- Sanata Shehu Buba zai horas da matasa 250 kan sana’ar gyaran takalma a jihar Bauchi
- Cibiyoyin kula da lafiyar kafafu da hannaye a Najeriya ta bude sabon ofishi a Kano
- Gwamnan Namadi ya amince da Mai Martaba Sarkin Kazaure a matsayin Amirul Hajj na jihar Jigawa
- Dalibai 41,000 da ba su kai shekara 16 ba sun yi rajistar JAMB ta shekarar 2025
- Za a fara gudanar da jarrabawar WAEC da NECO ta hanyar na’ura wato CBT
Kakakin rundunar yansanda na jihar, DSP Catherine Anene, wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin cikin wata sanarwa a madadin kwamishinan yansanda, Mukaddas Garba, yace an kaiwa yansanda rahoton aukuwar hatsarin a jiya da misalin karfe 2 da rabi na rana.