Tinubu ya kori manyan jami’an da ya gada daga tsohuwar gwamnatin data gabata

0 177

Shugaban kasa  Bola Ahmad Tinubu ya kori shugaban Hukumar sanya idanu akan hada-hadar kasuwanci ta Najeriya FCCPC, Mista Babatunde Irukera da Darakta-Janar kuma shugaban hukumar BPE (Bureau of Public Enterprises), Alexander Ayoola Okoh.

A wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya fitar a ranar Litinin.

Sanarwar ta bayyana cewa an umurci shugabannin da aka kora da su mika ragamar aikin su ga  manyan jami’ai a hukumominsu, har sai an nada sabbin shugabannin zartarwa.

Fadar shugaban kasar ta ce bisa wannan umarnin na shugaban kasa, tsige su daga mukamansu ya fara aiki nan take.

Leave a Reply

%d bloggers like this: