Wata kotun shari’ar musulunchi a Kano ta bayar da umarnin cigaba da tsare wani mutum saboda satar katan-katan na Maggi

0 76

Wata kotun Shari’ar Musulunchi a Kano ta bayar da umarnin cigaba da tsare wani mutum mai shekaru 37 mai suna Yusha’u Ado, saboda satar katan-katan na Maggi.

Mutumin wanda mazaunin Unguwar Goron Dutse ne dake Kano, yana fuskantar tuhume-tuhume biyu da suka hada da cin amana da sata.

Wanda ake kara ya amsa laifinsa.

A wani labarin kuma, ‘yansanda a jihar Kano sun kama wasu mutane 3 masu satar dabbobi da suka addabi mazauna kauyen Aujarawa Alkali a yankin karamar hukumar Gezawa.

Kakakin ‘yansanda na jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, yace bincike ya jawo an kama wanda yake sayen dabbobin da barayin suka sato.

Leave a Reply

%d bloggers like this: