

Latest posts by Sawaba FM (see all)
- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Wata kotun Shari’ar Musulunchi a Kano ta bayar da umarnin cigaba da tsare wani mutum mai shekaru 37 mai suna Yusha’u Ado, saboda satar katan-katan na Maggi.
Mutumin wanda mazaunin Unguwar Goron Dutse ne dake Kano, yana fuskantar tuhume-tuhume biyu da suka hada da cin amana da sata.
Wanda ake kara ya amsa laifinsa.
A wani labarin kuma, ‘yansanda a jihar Kano sun kama wasu mutane 3 masu satar dabbobi da suka addabi mazauna kauyen Aujarawa Alkali a yankin karamar hukumar Gezawa.
Kakakin ‘yansanda na jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, yace bincike ya jawo an kama wanda yake sayen dabbobin da barayin suka sato.