

Latest posts by Sawaba FM (see all)
- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Kungiyar kare hakkin dan adam ta Human Rights Watch ta ce auren wuri yana karuwa a kasarnan ne saboda gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihohi ba su dauki wata doka ta hana shi ba.
A wata sanarwa da kungiyar ta fitar ta ce Najeriya ce kan gaba a nahiyar Afirka wajen aurar da yara mata da wuri.
Kodayake dokar kare hakkin yara ta shekarar 2003 da gwamnatin tarayya ta yi, ta haramta aurar da yara ‘yan kasa da shekara 18.
Sai dai jihohin kasarnan da ke amfani da tsarin shari’ar musulunci sun gaza amfani da dokar da gwamnatin tarayya ta yi a kan batun aurar da yara ‘yan kasa da shekara 18.