Ma’aikatar ilimi ta jihar Zamfara ta sanar da sake bude makarantu

0 75

Ma’aikatar ilimi a jihar Zamfara ta sanar da sake bude makarantu a yau Litinin.

Cikin wata sanarwa da ma’aikatar ta fitar ta sanar da cewa za a bude makarantun firamare da na sakandire a yau.

Kazalika sanarwar ta ce makarantun gaba da sakandire kuma za su kasance a rufe har sai yanayin tsaro ya inganta.

A watannin baya ne aka rufe makarantun jihar saboda matsalolin tsaron da ake ci gaba da fuskanta ciki har da satar dalibai.

Leave a Reply

%d bloggers like this: