Yan sandan jihar Jigawa sun kama wasu mashahuran masu safarar miyagun kwayoyi su hudu a Hadejia

0 82

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta kama wasu mashahuran masu safarar miyagun kwayoyi su hudu a wani samame da aka kai zuwa maboyar bata gari a masarautun Hadejia da Kazaure.

Kakakin rundunar, ASP Lawan Shiisu Adam ya tabbatar da kamen a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai yau a Dutse.

Ya ce kamen ya biyo bayan umarnin kwamishinan ‘yan sandan jihar ne na kakkabe maboyar masu aikata miyagun laifuka a fadin jihar.

A cewar sanarwar, an kama wasu dilolin miyagun kwayoyi su biyu a jiya, yayin da aka kai wani samame zuwa wajen da ake zargin maboyarsu ce a kasuwar Malam Madori, bayan samun bayanan sirri.

Ya kara da cewa an damke sauran dilolin miyagun kwayoyin su biyu a Kofar Tasha dake karamar hukumar Kazaure.

Ya ce za a gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike.

Leave a Reply

%d bloggers like this: