Shugaba Buhari ya kaddamar da kwamitin gudanarwar kamfanin mai na NNPC

0 78

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar da kwamitin gudanarwar kamfanin mai na kasa NNPC.

Da yake kaddamar da kwamitin karkashin jagorancin Sanata Margery Chuba Okadigbo a fadar shugaban kasa a yau a Abuja, shugaban kasar ya umarce su da su mayar da hankali wajen samun riba tare da gudanar da aiki daidai da takwarorinsu na kamfanonin man fetur a fadin duniya.

Shugaban kasar ya tunatar da ‘yan kwamitin cewa an samar da su ne a sakamakon sauye-sauyen da dokar masana’antar man fetur ta gabatar na neman mayar da harkar man fetur a Najeriya zuwa hannun ‘yan kasuwa da kuma bin kyakkyawan tsarin kasuwanci a duniya.

A nasa jawabin, karamin ministan albarkatun man fetur, Timipre Sylva, ya ce a karkashin wannan gwamnati an samu nasarori da dama a harkar man fetur da suka hada da sanya hannu kan dokar masana’antar man fetur, rajistar kamfanin NNPC da kuma kaddamar da kwamitin gudanarwar kamfanin NNPC.

Leave a Reply

%d bloggers like this: