Asusun IMF ya gargadi gwamnatin tarayya da ta cire tallafin man fetur da wutar lantarki

0 158

Asusun ba da lamuni na duniya IMF ya gargadi gwamnatin tarayya da ta cire abin da ta kira tallafin man fetur da wutar lantarki a fakaice.

A cikin wani rahoto da IMF ta wallafa kwanan nan, kungiyar tabayyana cewa tallafin zai karkata akalar kashi uku cikin 100 na GDPn kasar nan a shekarar 2024 sabanin kashi daya cikin dari a shekarar da ta gabata.

A halin da ake ciki kuma, kiran da IMF ta yi na cire tallafin wutar lantarki na zuwa ne a daidai lokacin da ‘yan Najeriya ke zanga-zangar neman ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu, da ya mayar da kudin fito na Band A kamar yadda yake a halin yanzu.

Leave a Reply

%d bloggers like this: