

- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya fice daga wajen babban taron jam’iyyar APC mai mulki.
Shugaban kasar ya fice ne bayan ya gabatar da jawabinsa a wajen zaben fidda gwanin.
Kafin tafiyar sa, shugaba Buhari ya shaidawa ‘ya’yan jam’iyyar da su kasance masu hadin kai, kuma su guji tayar da zaune tsaye.
Ya kuma ce akwai bukatar jam’iyyar ta zabi shugabannin da za su ci gaba da dorawa akan ayyukansa na alkhairi.
Shugaban ya ce, dole ne wanda zai lashe zaben fidda gwanin ya zama mai ilimi, mai kishin kasa mai adalci mai tsananin imani da hadin kan kasa da karfin hali da manufa don ciyar da kasar gaba.
Ya taya murna ga wadanda tuni suka samu tikitin takara a jam’iyyar domin zaben 2023, ya kuma bukace su da su yi fice wajen cin nasara, musamman ga abokan takararsu da suka kayar a zaben fidda gwani.