

- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Hukumar kula da yanayi ta Najeriya, NIMet, ta yi hasashen samun hasken rana da gajimare daga ranar Litinin zuwa Laraba a fadin kasar.
Hasashen yanayi na da aka fitar jiya a Abuja ya yi hasashen cewa yankin arewa zai yi rana a yau tare da gajimare kadan tare da yiwuwar Tsawa da safe a sassan jihar Kebbi.
A cewar hukumar, za’asamu tsawa a sassan kudancin jihohin Borno, Kebbi, Kaduna, Gombe, Bauchi, Taraba da kuma Adamawa daga ranar Litinin zuwa Laraba da rana da kuma yamma.
Hukumar ta yi hasashen cewa yankin Arewa zai fuskanci hasken rana a ranar Talata da gajimare a safiyar ranar.
Hukumar ta kuma yi hasashen cewa za a yi Tsawa a wasu sassan Jihohin Kebbi, Jigawa, Bauchi, Gombe, Yobe, Taraba da kuma jihar Adamawa.