Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta yi gargadin cewa babu wani mutum da zai yi zabe matukar ba’a tantance shi ba

0 65

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta yi gargadin cewa babu wani mutum da zai yi zabe matukar ba’a tantance shi.

Sabon Kwamishinan Hukumar a Jihar Jigawa Farfesa Muhammad Lawan Bashar, shine ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Dutse.

A cewarsa, hukumar zata fara Kafe Rijistar masu zabe daga ranar 12 zuwa 25 ga watan Nuwamba na wannan shekara.

Kwamishinan Hukumar ya ce za’a kafe Rijistar a dukkanin Mazabu da Kananan Hukumomin Jihar Jigawa.

Haka kuma ya ce kafe Rijistar zai bawa mutane damar gano sunayen da suka yi amfani da shi a lokacin Rijistar zaben.

Farfesa Lawan Bashar, ya shawarci mutane su ziyarci Mazabun su da Kananan Hukumomin su domin ganin hotunan su da kuma sunayen da zasu bayyana a jikin katunan zaben su.

Leave a Reply

%d bloggers like this: