INEC ta kaddamar da guraren sabbin rumfunan zabe guda dubu 56 da 872 da aka kirkira.

0 99

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a yau tace ta cire rumfunan zabe daga guraren da basu dace ba, da guraren ibada a fadin kasarnan.

Shugaban hukumar, Mahmood Yakubu, ya sanar da haka a wata ganawa da kwamishinonin zabe na hukumar a Abuja.

A wajen ganawar, ya kaddamar da guraren sabbin rumfunan zabe guda dubu 56 da 872 da aka kirkira, tare da sanar da wasu shirye-shiryen zabe.

Bayan kirkirar sabbin rumfunan zaben, a yanzu Najeriya na da rumfunan zabe tsayayyu guda dubu 176 da 846, kari daga wadanda ake dasu a baya guda dubu 119 da 974 a jihoshin kasarnan 36 da babban birnin tarayya, Abuja.

Ya bayyana cewa jumillar rumfunan zabe 749 aka fitar daga guraren da basu dace ba.

Shugaban hukumar yace daga yanzu an dena amfani da rumfunan zabe na wucin gadi a Najeriya.

Leave a Reply

%d bloggers like this: