

- Anyi hasashen samun ruwan sama hade da tsawa a fadin kasarnan daga yau zuwa ranar Laraba - August 23, 2021
- Wata kungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaka da zasu fafata yaki da yan Taliban a Afghanistan - August 23, 2021
- ‘Yan bindiga sun kashe mutane 4 tare da sace wasu 50 a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara - August 23, 2021
Kwamatin lafiya na majalisar dokokin jihar Jigawa yaja hankalin jami’an tsaro dake kula da kan iyakar jihar Jigawa da Yobe a garin Birniwa da su rubanya kokari wajen tabbatar da ganin cewa matafiya daga jihohin Borno da Yobe ba su hauro zuwa Jigawa ba, domin dakile yaduwar cutar corona.
Shugaban kwamatin, Alhaji Aliyu Ahmad Aliyu, ya bayyana bukatar hakan lokacin da ya jagoranci ‘yan kwamatin zuwa ziyara kan iyakar a garin Birniwa.
Shugaban wanda ya mika kyallayen rufe fuska da hanci da sinadaran wanke hannu ga jami’an tsaro dake kula da kan iyakar, yace sun ziyarci yankin ne domin tabbatar da cewa jami’an tsaro da ma’aikatan lafiya na gudanar da ayyukansu kamar yadda ya kamata.
Aliyu Ahmad Aliyu ya yabawa baturen ‘yan sanda na yankin, Mustapha Muhammad Lawan bisa sadaukar da kai a aikinsa.
Daga nan sai yayi kira ga shugaban karamar hukumar Birniwa, Alhaji Muhammad Jaji Dole ya samar da kayan aikin da ake bukata ga jami’an tsaron.