Kwamitin zakka na masarautar Hadejia ya kaddamar da rabon zakka ta bana

0 231

A jawabinsa shugaban kwamitin zakka na masarautar Barista Abdulfatah Abdulwahab ya bukaci masu hali a cikin alumma dasu rinka bada zakka domin tsarkake dukiyoyinsu

Shugaban wanda ya samu wakilcin babban limamin Hadejia Mallam Yusif Abdulrahman Ya’u yace ana raba zakka a inda aka tara ta dan haka ya shawarci wadanda suka sami zakkar dasu yi amfani da ita ta hanyar data dace

Rabon da aka yi a gonar Adamu Maje dake garin Hadejia, a yayin jawabinsa sakataren kwamitin Injiniya Ismaila Garba Barde yace an raba zakkar shinkafa da masara da Dawa da aka bayar a matsayin zakka a gonar ga mabukata.

A jawabinsa daya daga cikin wadanda suka sami zakkar Malam Ibrahim Usman ya yaba da kokarin kwamitin na karba da kuma rabon zakka na masarautar.

Leave a Reply

%d bloggers like this: