Mutane 5 ne suka mutu yayin wata zanga-zanga a birnin Cape Town na kasar Afirka ta Kudu

0 282

Wadanda lamarin ya rutsa da su sun hada da wani dan kasar Birtaniya mai shekaru 40 da ma’aikatar harkokin wajen Birtaniya ke tallafa wa danginsa.

Yajin aikin na tsawon mako guda dai an fara gudanar da shi ne a matsayin martani ga abin da direbobin suka ce amfani da karfi na jami’an tsaro.

Direbobin tasi da masu motocin sun ce ana kai wa motocin su hari tare da daure su kan wasu kananan laifuka. Ma’aikatan tasi masu kananan bus a fadin Cape Town sun kuma nuna takaicin yadda gwamnati ke kame motocin da suka ce ba su dace da hanya ba.

Leave a Reply

%d bloggers like this: