Mutane na cigaba da rasa rayukansu sakamakon nau’in cutar korona ta Omicron a Birtaniya

0 87

Aƙalla mutum ɗaya ya rasu sakamakon nau’in cutar korona na Omicron a Birtaniya, a cewar Firaminista Boris Johnson.

Shugaban ya ce nau’in cutar ya kuma haddasa kwantar da mutane a asibiti, yana mai cewa “abu mafi muhimmanci” da mutane ya kamata su yi shine su je a jaddada musu rigakafi.

Da yakai ziyara  wani asibiti a Landan, Boris Johnson ya ce ya kamata mutane su daina tunanin cewa Omicron ƙaramin nau’i ne.

Firamistan ya ce abin takaici, da gaske Omciron na haddasa jinya a asibitoci kuma har mutum ɗaya ya mutu.

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ce bayyana fargaba kan yaduwar cutar, inda ta gargadi shugabannin Duniya su dauki matakan dakile yaduwar ta.

Leave a Reply

%d bloggers like this: