NNPC zai sayar da hannayen jarinsa a karon farko ga jama’a

0 72

Kamfanin Man Fetur na Kasa (NNPC) zai sayar da hannayen jarinsa a karon farko ga jama’a a cikin shekaru uku, wanda hanya ce ta tara kudaden shigar da ake bukata.

Shugaban kamfanin, Mele Kyari, ya fadawa kamfanin jaridar Bloomberg a cikin tattaunawar bidiyo yau cewa sayar da hannun jarin kamfanin a karon farko zai taimaka wa Najeriya ta ci gaba da kasancewar tare da kasashe masu arziki man fetur a duniya.

Kamfanin na NNPC a makon da ya gabata ya sanar da samun ribar Naira biliyan 287 a shekarar 2020, wanda shi ne na farko tun lokacin da aka kafa shi a shekarun 1970.

Najeriya ce kasa mafi yawan arzikin man fetur a nahiyar Afirka.

Amma arzikin baya nunawa akan rayuwar jama’ar kasarnan da yawansu ya kai sama da miliyan 200, inda mutane ke fama da matsanancin rashin aikin yi da bakin talauci.

Leave a Reply

%d bloggers like this: