Ƙungiyar ma’aikatan ƙananan hukumomi ta Najeriya (NULGE), reshen ƙaramar hukumar Birniwa, ta gudanar da zaɓen sabbin shugabanni da za su jagoranci ayyukan ƙungiyar na tsawon shekaru huɗu masu zuwa.
Comrade Ibrahim Musa – Shugaba
Musa Muhammad Kumsa – Mataimakin Shugaba
Sa’idu Abdullahi Birniwa – Sakatare
Garba Rabi’u – Ma’ajin Kuɗi
Hamza Muhammad – Mataimakin Sakatare
Ibrahim Muhammad – audito
Hadiza Musa Hassan – Shugabar mata
Da yake jawabi jim kaɗan bayan zaɓen, wakilin shugaban ƙungiyar na jihar Jigawa, Ibrahim Mu’azu Maigatari, ya shawarci sabbin shugabannin da su gudanar da aikinsu cikin gaskiya da rikon amana domin ci gaban ƙungiyar.
A nasa jawabin, shugaban ƙaramar hukumar Birniwa, Alhaji Shehu Baba Birniwa, ya bayyana jin daɗinsa kan yadda aka gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da adalci.
A cikin jawabin godiya, sabon shugaban ƙungiyar, Comrade Ibrahim Musa, ya yi alƙawarin yin aiki tare da hukumomi da masu ruwa da tsaki domin cimma burin da aka sa gaba.