Rundunar Sojin Sama Ta Najeriya Ta Kashe Fiye da ’Yan Ta’adda 40 A Jihar Borno

0 163

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ta ce ta kashe fiye da ’yan ta’adda 40 a hare-haren sama da aka kai a yankunan Azir da Musarram a jihar Borno.

Hare-haren, da aka aiwatar bisa sahihin bayanan sirri, sun dakile shirin kai farmaki kan al’ummomi.

Rundunar ta ce an kai jerin hare-hare ne bayan gano ’yan ta’adda suna ƙoƙarin sake taruwa a dazuka.

Hukumomi sun bayyana cewa yankunan sun samu natsuwa, tare da jaddada cewa za a ci gaba da matsa lamba kan masu tayar da ƙayar baya.

Leave a Reply