Jadawalin Gasar Kofin Duniya Ta 2026

0 17

An fitar da jadawalin wasannin Gasar Kofin Duniya ta 2026 da za a gudanar a ƙasashen Amurka da Mexico da Canada, wadda za ta fara a ranar 11 ga watan Yuni, 2026.

Za a fara gasar ne da wasan rukuni na A tsakanin Mexico da Afirka ta Kudu a birnin Mexico City ranar Alhamis, 11 ga watan Yuni da ƙarfe 7:00 na yamma agogon GMT.

A rana guda kuma, Koriya ta Kudu za ta kara da Jamhuriyyar Czech a birnin Guadalajara.

A ranar Asabar 13 ga watan Yuni, za a fafata tsakanin Brazil da Morocco a birnin East Rutherford.

Ita kuwa Jamus za ta kara da Curacao, yayin da Netherlands za ta fafata da Japan a ranar Lahadi 14 ga watan Yuni.

Sai kuma Spain da za ta kara da Cape Verde, yayin da Belgium za ta kara da Masar a ranar Litinin 15 ga watan Yuni.

Ƙasashen Afirka da za su haska a gasar
Daga cikin ƙasashen Afirka da za su fafata a gasar akwai Morocco da Masar da Ghana da Tunisia da Ivory Coast da Afirka ta Kudu da DR Congo da kuma Cape Verde.

Zagayen ‘yan 16
Za a fara wasannin zagayen ‘yan 32 ne daga ranar 28 ga watan Yuni, yayin da wasannin zagayen ‘yan 16 za su fara daga ranar 4 ga watan Yuli.

Za a gudanar da wasan kwata-final daga ranar 9 zuwa 11 ga watan Yuli, sannan wasan dab da na ƙarshe zai gudana a ranakun 14 da 15 ga watan Yuli.

Wasan Ƙarshe
Za a buga wasan ƙarshe na gasar ne ranar Lahadi 19 ga watan Yuli a birnin East Rutherford da ƙarfe 7:00 na yamma agogon GMT.

Rahotanni sun nuna cewa wannan ne karo na farko da ƙasashe uku za su haɗa kai wajen karɓar baƙuncin Gasar Kofin Duniya ta FIFA.

Leave a Reply