

- Wasu ‘yan bindiga sun kashe wakilai uku na ‘yan takarar gwamna na jam’iyyar PDP daga karamar hukumar Mariga ta jihar Neja - May 26, 2022
- Dalilan da yasa wasu ‘yan takarar gwamna 2 na jam’iyyar APC suka yi watsi da zaman ganawar da gwamna Badaru ya kira domin a samar da dan takarar daya tal - May 26, 2022
- Mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da aka dakatar, Abba Kyari ya garzaya wata babbar kotun tarayya domin neman belinsa - May 26, 2022
Rundunar yansandan jihar Jigawa ta tabbatar da kisan wani mutum guda wanda aka samu gawarsa a cikin daji yayin fada tsakanin makiyaya da manoma a jihar Jigawa.
Hakan na zuwa ne bayan wasu shaidun gani da ido sun ce akalla mutane 12 aka kashe yayin rikicin wanda ya auku a garuruwan Matarar Gamji da Madachi, dake yankin karamar hukumar Kirikasamma.
An rawaito cewa fadan ya fara ne yayin da makiyayan tare da shanunsu aka yi zargin sun mamaye gonaki tare da lalata amfanin gona a garuruwan biyu.
Wani da ya shaida rikicin da idonsa, Idris Madachi, ya gayawa manema labarai cewa makiyayan tare da shanunsu sun mamaye gonaki tare da lalata amfanin gona kuma hakan ya bakantawa manoman rai.
Da aka nemi jin ta bakinsa, kakakin yansandan jiha, ASP Lawan Shiisu Adam, ya tabbatar da aukuwar lamarin.