Fitaccen malamin addinin Musuluncin nan na jihar Kano, Malam Ibrahim Khalil, ya bayyana cewa jin waƙa yana ƙara nutsuwa, imani, ƙwazo da kuma zaburar da mutane.
Malam Khalil ya bayyana haka ne a ranar Lahadi a wajen maulidin Annabi Muhammad (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi) na gidan Sheikh Malam Nasidi Abubakar Goron Dutse dake unguwar Goron Dutse a cikin birnin Kano.
Malamin, wanda shi ne Shugaban Majalisar Malamai ta Jihar Kano, ya ce: “Shi yasa da idan ana aikin gayya a kan kirawo Shafi’u, wani babban mawaƙi na Kano, da shi da masu kaɗa masa ganga, ana kaɗawa ana gangi ana waƙa, a kawo kunu a sha.
- An tsare wani mataimakin ministan tsaron kasar Rasha bisa zargin karbar cin hanci
- An dakatar da Daraktan kwalejin Birnin Kudu da jami’in kula da harkokin abinchi na kwalejin
- Gwamna Namadi yayi kira ga sabbin masu yiwa kasa hidima da aka turo jihar jigawa da su kasance jakadu na gari
- Majalisar dokokin jihar Jigawa ta kafa kwamatin wucin gadi domin nazari kan dokar hukumar zabe
- Jam’iyyar PDP za ta gudanar da babban taronta a jihohi 25 domin zaben sabbin shugabanni
Wasu lokuta ma a afa wani abu– ka ji garau, to a lokacin kai bai waye ba a lokacin, sai a dama a cikin kunu su sha, ka gan shi yana ta tsalle, har da to haka ake yi.
“To wannan saboda ɗan Adam, shi yasa za ku ga a cikin Sahihul Bukhari, lokacin da aka zo ana yin Masallacin Annabi (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi), da lokacin da ake haƙa Ramin Gwalalo, to ana rera waƙa, to Annabi ba ya rera waƙa, amma su sahabbai suna rerawa”.