

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Shugaban Kasa Muhammadu Buhari zai jagoranci tawagar Najeriya zuwa taron shugabannin kasashe na kungiyar kasashe rainon Ingila wanda za a gudanar a Kigali, babban birnin kasar Rwanda, nan da mako mai zuwa.
Jakadan Rwanda a Najeriya, Stanislas Kamanzi, shine ya sanar da haka a wajen zaman ganawar shirye-shiryen taron da aka gudanar a Abuja.
Ya mika godiyarsa ga shugaban kasa Muhammadu Buhari bisa amsa gayyatar shugaban kasar Rwanda.
Za a gudanar da taron tsakanin ranakun 20 zuwa 26 ga watan da muke ciki.
Stanislas Kamanzi yace dandalin taron zai kasance wajen tattaunawa da daukar matakai masu muhimmanci da suka shafi rayuwar kowa, wadanda suka kun shi matakan dokoki da dorewar tattalin arziki, yanayi, lafiya, fasaha da kuma matasa.
Jakadiyar Burtaniya a Najeriya, Catriona Laing, tace Birtaniya yanzu a shirye take ta mika ragamar mulkin na kungiyar kasashe rainon Ingila ga kasar Rwanda bayan shekaru hudu.