Shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan ya bayyana cewa jam’iyyar APC mai mulki ta cika alkawuran da ta daukarwa ‘yan Najeriya

0 73

A jiya ne shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan ya bayyana cewa jam’iyyar APC mai mulki ta cika alkawuran da ta daukar ‘yan Najeriya.

Don haka Lawan ya roki ‘yan Najeriya da su sake baiwa jam’iyyar dama a 2023.

Ya ce jam’iyyar ta yi alkawarin yin duk mai yiwuwa wajen kyautata rayuwar su, inda ya ce ta cika alkawuran da ta dauka tun lokacin da ta hau mulki.

Ya bayyana haka ne a wani taro da aka yi a Ilorin babban birnin jihar.

Kafin hakan dai, Shugaban Majalisar Dattawan ya kaddamar da ginin wata cibiyar gyara ma’aikatan jinya da ke Asibitin na gwamnatin  Tarayya da ke Budo-Egba a Karamar Hukumar Asa, tare da kaddamar da Cibiyar Kula da Lafiyar Jama’a ta Idi-Isin a Unguwar Okolowo da ke Ilorin.

Leave a Reply

%d bloggers like this: