Sojoji a Mali sun maido da iko a sansanoni uku da ke tsakiyar kasar bayan da mayakan jihadi suka kai musu wani hari

0 55

Sojoji a Mali sun maido da iko a sansanoni uku da ke tsakiyar kasar bayan da mayakan jihadi suka kai musu hari a lokaci guda.

A cewar sanarwar Sojoji 6 ne suka mutu sannan aka kashe mayakan makiya 11.

An kuma kai wani sabon hari a makwabciyar kasar Burkina Faso.

Wadannan hare-hare guda hudu na masu jihadi sun nuna yadda dakarun soji ke da rauni a yankin Sahel.

A yayin da wasu ‘yan kunar bakin wake ke tuka motoci cike da bama-bamai su tunkari sansanonin sojoji a yankin Mopti na kasar Mali.

Wannan na zuwa ne adaidai lokacin da wata kungiyar masu da’awar jihadi take kashe sojoji da fararen hula a kan iyakar Arewacin Burkina Faso.

Kafin hakan dai, sojojin kasashen biyu, sun kwace mulki bayan da suka zargi zababbun gwamnatocin fararen hula da kasa tinkarar masu jihadi.

Leave a Reply

%d bloggers like this: