

- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Sojoji a Mali sun maido da iko a sansanoni uku da ke tsakiyar kasar bayan da mayakan jihadi suka kai musu hari a lokaci guda.
A cewar sanarwar Sojoji 6 ne suka mutu sannan aka kashe mayakan makiya 11.
An kuma kai wani sabon hari a makwabciyar kasar Burkina Faso.
Wadannan hare-hare guda hudu na masu jihadi sun nuna yadda dakarun soji ke da rauni a yankin Sahel.
A yayin da wasu ‘yan kunar bakin wake ke tuka motoci cike da bama-bamai su tunkari sansanonin sojoji a yankin Mopti na kasar Mali.
Wannan na zuwa ne adaidai lokacin da wata kungiyar masu da’awar jihadi take kashe sojoji da fararen hula a kan iyakar Arewacin Burkina Faso.
Kafin hakan dai, sojojin kasashen biyu, sun kwace mulki bayan da suka zargi zababbun gwamnatocin fararen hula da kasa tinkarar masu jihadi.