Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa Iyorchia Ayu ya tabbata dan takarar kujerar shugaban jam’iyyar PDP na kasa

0 61

Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa Iyorchia Ayu ya zama dan takarar kujerar shugaban jam’iyyar PDP na kasa.

Zabin nasa ya zo ne bayan wani zaman ganawar ‘ya’yan jam’iyyar PDP na Arewa wanda aka yi a gidan gwamnan jihar Bauchi dake unguwar Asokoro dake Abuja.

A wani labarin kuma, Jam’iyyar PDP a jihar Zamfara a yau ta koka kan shirin rusa helkwatarta ta jiha, wanda hukumar tsare-tsaren birane da yankuna ta jihar Zamfara ke shirin yi.

Sakataren Yada Labaran jam’iyyar a jihar, Alhaji Farouk Ahmad Shattima, ya shaidawa manema labarai cewa bayan gwamna Bello Mohammed Matawalle ya koma jam’iyyar APC, an karbe helkwatar PDP inda aka yi mata fenti da tambarin APC.

Sai dai, ba a samu damar jin ta bakin jami’an hukumar tsare-tsaren birane da yankuna ta jihar Zamfara ba, har zuwa lokacin da ake hada wannan labarin.

Leave a Reply

%d bloggers like this: