Wata zanga-zanga ta barke a jihar Katsina, bisa kisan wasu mutum 5 da jami’an kwastan suka yi

0 99

Wata zanga-zanga ta barke yau a Jibiyan jihar Katsina, bisa kisan wasu mutane 5 da jami’an kwastan suka yi lokacin da suke kokarin kama masu fasa kwaurin shinkafa a yankin.

Shaidun gani da ido sun ce wasu dayawa daga cikin wadanda lamarin ya rutsa da su, sun samu raunuka kuma suna karbar magani a wani karamin asibiti.

Shaidun sun ce motar jami’an kwastan ta bi ta kan wani gungun mutane, a lokacin da suke gudu a kokarinsu na kama masu fasa kwaurin shinkafa, inda suka kashe mutane 5 tare da jikkata wasu da dama.

Kakakin yansandan jihar Katsina, Gambo Isah, bai amsa kiran wayarsa ba domin magana akan lamarin.

Sai dai, jami’in hulda da jama’a na hukumar kwastan a jihar Katsina, Danbaba Isah, ya musanta cewa jami’an hukumar suna bin sahun wata mota ne.

Danbaba Isa yayi kira ga jama’a da su kauracewa yada labaran da basu tabbatar ba.

Leave a Reply

%d bloggers like this: