

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Shugaban Kungiyar Gwamnonin Arewa ta Tsakiya Kuma Gwamnan Jihar Neja Alhaji Abubakar Sani Bello, ya bukaci Sojojin Najeriya su ninka kokarin su domin dakile ta’addanci a Jihar kamar yadda Shugaba Buhari ya basu umarni.
Gwamnan ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa biyo bayan karuwar hare-haren ta’addanci a Kananan hukumomin Shiroro da Munya da Rafi da kuma Paikoro na Jihar.
Gwamnan ya bayyana damuwa kan yadda yan bindigar suke cigaba da kaiwa hare-hare a sassan Jihar wanda hakan ne ya sa ake samun asarar rayuwa da Dukiyoyin Al’umma, ciki harda Sojoji.
A cewarsa, karuwar hare-haren yan bindigar a Jihar Neja, na cigaba da dakile kokarin hukumomin tsaro a yankin.
A kwanakin baya Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya umarci Sojoji su ninka kokarin su wajen murkushe yan bindigar gaba daya.