An sace wani tsohon dan majalisar dokokin jihar Jigawa, Haladu Bako.
Mansur Ahmed, hadimin tsohon gwamnan Jigawa, Sule Lamido, ya ce an sace Haladu Bako ne a daren jiya yayin da yake tafiya daga Kano zuwa jihar Jigawa.
Mansur Ahmed ya tunatar da cewa Haladu Bako ya wakilci karamar hukumar Auyo a majalisar dokokin jiharnan daga shekarar 2007 zuwa 2015.
Haladu Bako, jigo a jam’iyyar PDP a jihar Jigawa, ya sake tsayawa takara amma ya rasa kujerar a zaben shekarar 2019.
Lokacin da aka tuntubi kakakin ‘yan sandan Jihar Jigawa, Lawan Shisu Adam ya ce har yanzu ba shi da labarin abin da ya faru.
Ba a fiye samun matsalar satar mutane domin neman kudin ba a nan jihar Jigawa.
Sai dai, manazarta sun yi gargadin cewa tabarbarewar rashin tsaro da ke faruwa a yankin Arewa maso Yamma na iya jawo matsalar zuwa jiharnan.