Yadda aka sace tsohon dan majalisar dokokin jihar Jigawa

0 86

An sace wani tsohon dan majalisar dokokin jihar Jigawa, Haladu Bako.

Mansur Ahmed, hadimin tsohon gwamnan Jigawa, Sule Lamido, ya ce an sace Haladu Bako ne a daren jiya yayin da yake tafiya daga Kano zuwa jihar Jigawa.

Mansur Ahmed ya tunatar da cewa Haladu Bako ya wakilci karamar hukumar Auyo a majalisar dokokin jiharnan daga shekarar 2007 zuwa 2015.

Haladu Bako, jigo a jam’iyyar PDP a jihar Jigawa, ya sake tsayawa takara amma ya rasa kujerar a zaben shekarar 2019.

Lokacin da aka tuntubi kakakin ‘yan sandan Jihar Jigawa, Lawan Shisu Adam ya ce har yanzu ba shi da labarin abin da ya faru.

Ba a fiye samun matsalar satar mutane domin neman kudin ba a nan jihar Jigawa.

Sai dai, manazarta sun yi gargadin cewa tabarbarewar rashin tsaro da ke faruwa a yankin Arewa maso Yamma na iya jawo matsalar zuwa jiharnan.

Leave a Reply

%d bloggers like this: