Rundunar yan Sandan Jihar Jigawa ta bayyana cewa wani Matashi dan shekara 25 mai suna Nura Muhammad, ya rataye kansa a kyauyen Chamo na karamar hukumar Dutse.
Kakakin Rundunar na jihar Jigawa ASP Lawan Shiisu Adam, shine ya tabbatar da hakan ga Kamfanin Dillancin Labarai na Kasa NAN a Dutse.
A cewarsa, mutumin wanda yake zaune a kyauyen Chamo, ya rataye kansa ne da misalin karfe 12:30 na Rana a dakin sa.
ASP Lawan Shiisu Adam, ya ce tun da farko mutumin ya fadawa matarsa cewa, akwai yuwuwar mutuwarsa a nan gaba.
Kakakin rundunar yan sandan ya ce Matar marigayin, ta fadawa yan sanda cewa mijin nata yana fama da tabuwar hankali, tun bayan daya dawo daga jihar Lagos a watan Yuli.
Kazalika ya ce bayan faruwar lamarin ne aka dauki gawar mutumin, zuwa babban Asibitin Dutse, domin yin gwaje-gwaje, inda likita ya tabbatar da musuwarsa.