‘Yan sanda sun kama shanu 25 da ake zargin an sace su a Jihar Sakkwato

0 514

Ofishin ‘yan sanda reshen Gada a Jihar Sakkwato ta kama shanu 25 da ake zargin an sace su daga bata gari.
An same su ne a cikin dajin da ke iyaka da Karamar Hukumar Sabon Birni a jihar ranar Alhamis, bayan samun bayanai daga hukumomin yankin.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Ahmad Rufai, ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa a ranar Juma’a.
Ya ce an fara dawo da shanun ne bayan wani mai suna Alhaji Muhammad Kyari ya bayar da rahoton shanun da suka bata.
Sanarwar ta ce, “Hakimin Gada, Alhaji Idi tsohon dagacin kauyen Gidan Rabami a karamar hukumar Gada, tun da farko ya sanar da hukumomi game da batan shanun.
Sanarwar ta kara da cewa bayan kammala aikin dawo da shanun, an kai su ofishin yan sanda dake Gada, inda ake tsare da su cikin tsaro.
‘Yan sanda sun yi kira ga duk wani mai dabbobi da shanunsa suka bata da ya je ofishin ‘yan sanda tare da sahihin shaidar mallaka domin tantancewa da karɓar shanunsa.
Hukumomi kuma suna karfafa wa mazauna Gada da makwabtan unguwanni da su yada wannan bayani sosai domin hanzarta tantance shanun da hana rikici ko jinkiri wajen mayar da su ga masu su.

Leave a Reply