Ƴan bindiga sun kashe mutum 7 kuma sun babbake gidaje 250 a masarautar Miango dake karamar hukumar Bassa ta jihar Filato.
Ƴan bindigan sun kai wa masarautar hari ne a daren Asabar.
Sakataren yaɗa labaran kungiyar Iregwe Davidson Malison ya sanar da haka ranar Lahadi a garin Jos.
Malison ya ce maharan sun lalata gonaki sama da 40 a masarautar.