

Latest posts by Sawaba FM (see all)
- Anyi hasashen samun ruwan sama hade da tsawa a fadin kasarnan daga yau zuwa ranar Laraba - August 23, 2021
- Wata kungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaka da zasu fafata yaki da yan Taliban a Afghanistan - August 23, 2021
- ‘Yan bindiga sun kashe mutane 4 tare da sace wasu 50 a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara - August 23, 2021
Kungiyar masu sana’ar fawa ta kasa reshen jihar Jigawa, ta yabawa karamar hukumar Auyo bisa daga darajar gidan mayankar dabbobi ta karamar hukumar.
Alhaji Adamu Dan- Sifiringa mai Magana da yawun kungiyar ya bayyana hakan ga manema labarai a garin Auyo. Yace mayankar ta garin Auyo ta lalace ne tun kafin ruwan sama ya kara lalata a shekarar 2018.
Dan-Sifiringa ya kara da cewa mayankar yanzu ta kasance ta zamani inda take dauke da kayayyaki masu inganci da nagarta.