- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Akalla mutane 5 aka kashe yayin da wasu da dama suka jikkata a mummuna rikicin da ya auku tsakanin manoma da makiyaya a yankin karamar hukumar Guri ta jihar Jigawa.
An rawaito cewa gomman mutane sun jikkata a rikicin, wanda aka ce ya auku ne sanadiyyar rashin jituwa tsakanin bangarorin biyu.
A cewar wani ganau, lamarin da auku a ranar kasuwar mako ya jawo mutuwar wani mutum guda, inda ya haifar da harin ramuwar gayya.
Ana yawan samun rikici a kananan hukumomin Guri, Kirikasamma da Birniwa tsakanin manoma da makiyaya.
Da yake tabbatar da aukuwar lamarin, kakakin rundunar ‘yansandan jihar Jigawa, Lawan Shiisu Adama, yace Fulani makiyaya da manoma sun yi rikici a dajin Magirami dake karamar hukumar Guri, inda ya kara da cewa tuni jami’an yansanda karkashin jagorancin DPO na Guri suka ziyarci wajen domin wanzar da zaman lafiya.