

Latest posts by Sawaba FM (see all)
- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Gwamnatin Jihar Kaduna a yau ta ayyana dokar ta baci tsawon awanni 24 a kananan hukumomin Jema’a da Kaura na jihar.
Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gid ana jihar, Samuel Aruwan, ya sanar da haka cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Kaduna.
Samuel Aruwan yace biyo bayan shawarwarin daga hukumomin tsaro, gwamnatin jihar Kaduna ta ayyana dokar hana fita kwata-kwata a kananan hukumomin Jema’a da Kaura na jihar ba tare da bata lokaci ba.
Ya kara da cewa an bawa hukumomin tsaro damar tabbatar da dokar.
Kwamishinan yace za a sanar da Karin bayani idan an samu bukatar hakan.