- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Kwamishiyar tarayya ta hukumar kula da ‘yan gudun hijira, Imaan Sulaiman Ibrahim, tace akwai ‘yan Najeriya kimanin dubu 300 dake gudun hijira a jamhuriyar Nijar.
Tace akwai wasu dubu 20 a Chaid da dubu 180 a Kamaru, amma adadin zai iya raguwa kasancewar an fara aikin dawo da su gida.
Ta kuma ce an fara sanya ido akan ayyukan kungoyiyi masu zaman kansu domin magance cin amanar aikinsu a guraren da ake rikici.
Imaan Sulaiman Ibrahim, yayin wata ziyara zuwa helkwatar kamfanin Media Trust a Abuja dake wallafa jaridar Daily Trust da Aminiya, tace an bawa ma’aikatar jin kai, kula da annoba da walwalar jama’a ikon amincewa da ayyukan kungoyiyi masu zaman kansu, domin su dace da kudirorin gwamnati.
Ta kara da cewa matsalolin kungoyiyi masu zaman kansu sun sanya wasu gwamnatocin jihoshi kin amincewa da ayyukansu a jihoshinsu.