Hukumar Alhazai ta Kasa ta bayar da sanarwar kawo karshen jigilar maniyyata daga Najeriya zuwa aikin Hajjin Bana a Saudiyya.
Sanarwar na cikin jawabin da aka bawa kamfanin dillancin labarai, daga hannun shugaban sashen hulda da jama’a ta hukumar, Fatima Usara, jim kadan bayan jigilar karshe a jirgin karshe wanda ke dauke da ma’aikatan hukumar, sa’ilin da suka tashi daga filin jiragen sama Nnamdi Azikiwe dake Abuja, zuwa Saudiyya.
A cewar Fatima Usara, aikin hajjin bana, ya kunshi jigilar alhazai a jirage sau 93, wadanda suka kai alhazai 44,450, daga hukumomin jin dadin alhazai na jishoshi.
![](https://i0.wp.com/www.sawabafm.com/wp-content/uploads/2019/08/Hajji-Makka.jpg?resize=680%2C454&ssl=1)
Hukumar ta kuma yabawa kokarin hukumomin jin dadin alhazai na jishoshi da sauran masu ruwa da tsaki, domin nasarar aikin da aka samu.
A cewarta, hukumar tana fatan sake samun makamanciyar nasarar da aikin hadin gwiwa, yayin aikin dawo da alhazan gida.