

- Anyi hasashen samun ruwan sama hade da tsawa a fadin kasarnan daga yau zuwa ranar Laraba - August 23, 2021
- Wata kungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaka da zasu fafata yaki da yan Taliban a Afghanistan - August 23, 2021
- ‘Yan bindiga sun kashe mutane 4 tare da sace wasu 50 a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara - August 23, 2021
Cibiyar dakile yaduwar cututtuka ta Najeriya ta samar da wajan gwajin kwayar cutar COVID-19 a asibitin koyarwa na jami’ar Maiduguri, domin kula da kuma kaucewa yaduwar ctar COVID-19 yankin arewa maso gabas.
Babban daraktan Asibitin, Farfesa Ahmad Ahidjo, shine ya bayar da tabbacin hakan ciki wata ganawa da yayi da kamfanin dillancin labarai na kasa, a yau Alhamis a Maiduguri.
Farfesa Ahmad ya bayyana cewa, haka kuma Asibitin zai iya gwada wanda ake zargin yana dauke da kwayar cutar dake Borno, Yobe, Adamawa da wasu jihohin da ke makotaka da su.
Haka kuma ya kara da cewa asibitin ya dauki matakan kare yaduwar cutar, tare da kiyaye lafiyar maras lafiya, ma’aikata da kuma masu ziyara.