“Ana kaiwa Gidajen gyaran halayya hare-hare domin a kunyata gwamnatin tarayya” a cewar Ministan Harkokin Gida
Ministan Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida Mista Rauf Aregbesola ya bayyana cewa ana kaiwa Gidajen gyaran halayya hare-hare domin a kunyata gwamnatin tarayya.
A cikin yan watannin nan akan yawan kaiwa gidajen gyaran halayya hare-haren inda aka saki daurarru tare da kashe Jami’an tsaro.
Hari na baya-bayan nan shine wanda aka kai ranar Juma’a a gidan gyaran halayya na Abologo ta Jihar Oyo, wanda wasu yan bindiga suka kai.
Da yake jawabi a Jiya lokacin da yake duba gidan gyaran halayyar Ministan ya ce gwamnati zata hukunta wanda suka kai harin.
A cewarsa, hare-haren da ake kaiwa gidajen gyaran halayyar shiryayyen abune wanda ake kitsawa domin bata gwamnati a Idon Jama’a.
Ya ce gwamnatin tarayya zata kamo masu kaiwa hare-haren harda kuma mutanen da suke tserewa daga gidajen.
Kazalika, ya ce tuni suka fara kama wadanda suka gudu daga gidajen, kuma zasu cigaba da kama sauran wadanda suka gudu.