

- Anyi hasashen samun ruwan sama hade da tsawa a fadin kasarnan daga yau zuwa ranar Laraba - August 23, 2021
- Wata kungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaka da zasu fafata yaki da yan Taliban a Afghanistan - August 23, 2021
- ‘Yan bindiga sun kashe mutane 4 tare da sace wasu 50 a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara - August 23, 2021
Gwamnonin kasarnan 36, sunyi alkawarin aiki tare da sabon shugaban ma’akatan fadar shugaban kasa Farfesa Ibrahim Gambari.
Cikin wasikar taya murna da kungiyar gwamnonin ta aike, mai dauke da kwanan watan 18 ga Mayun shekarar da muke ciki, dauke da sa hannun shugaban kungiyar kuma gwamnan jihar Ekiti Kayode Fayemi, sunce hakan ya zama wajibi, musamman duba da karyewar farashin mai da cutar corona tayi sanadi.
Gwamnonin dai cikin wasikar da suka aikewa Gambari, sun bayyana farin cikinsu kan nadin nasa, duba da cancantarsa, bisa gogayya da kuma kwarewar aiki da yake da ita.
Haka kuma sunyi fatan nasara gareshi, wajen gudanar da ayyukansa cikin yanayi dake tattare da kalubale.