Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona ta shirya sauraron tayin masu bukatar yan wasan ta har kusan 12 da zarar an bude kakar wasanni ta bana.
Tuni har masu sharhin wasanni suka fara alaƙanta cefanar da yan wasan ne saboda kokarin kawo dan wasan gaba na Inter Milan Lautaro Martinez.
Daga cikin yan wasan da za a kadawa kararrawar dai akwai; Dembele da Coutinho, Samuel Umtiti, Junior Firpo, Ivan Rakitic, Neto, Nelson Semedo, Arturo Vidal, Martin Braithwaite, Carles Alena, Rafinha Alcantara da kuma Jean-Clair Todibo.
- Ina alfahari da samun dimbin goyon bayan da ake bukata domin zama ‘yartakara – Kamala Harris
- An bukaci mazauna jihar Jigawa da su kula da matakan kariya domin dakile ambaliyar ruwa
- Ƙasashe 58 sun goyi bayan Ngozi Okonjo-Iweala ta yi tazarce a Shugabar Kungiyar Cinikayya ta Duniya
- Kungiyar Kwadago ta yi gargadi kan yunkurin dakushe zanga-zangar da ake shirin yi a fadin kasar
- Gwamnatin Tarayya ta gabatar da buƙatar ƙarin Naira tiriliyan 6.2 akan kasafin kuɗin bana
Shugaban ƙungiyar Jose Bartomeu ya zanta da mahukunta a kungiyar Inter Milan din kan ɗaukar ɗan wasan ɗan asalin ƙasar Argentina.
Barcelona dai na cikin ƙaƙanakayi ta fuskar samun kuɗin shiga sanadiyyar annobar Korona, don haka kuɗin da zasu kashe ba shi da yawa kan yan wasa.
Jaridar Marca ta rawaito cewa Barcelona zata sanya kusan rabin yan wasanta a kasuwa don samun kuɗaɗen shiga da kuma samun zarafin kawo sabbin fuska kungiyar.
Amma sai dai sanarwar ta bayyana cewa ba duk yan wasan 12 ne zasu tafi a matsayin tafiyar din-din ba, wasu daga cikinsu zasu tafi ne a matsayin aro.