

Latest posts by Sawaba FM (see all)
- Wasu ‘yan bindiga sun kashe wakilai uku na ‘yan takarar gwamna na jam’iyyar PDP daga karamar hukumar Mariga ta jihar Neja - May 26, 2022
- Dalilan da yasa wasu ‘yan takarar gwamna 2 na jam’iyyar APC suka yi watsi da zaman ganawar da gwamna Badaru ya kira domin a samar da dan takarar daya tal - May 26, 2022
- Mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da aka dakatar, Abba Kyari ya garzaya wata babbar kotun tarayya domin neman belinsa - May 26, 2022
Cibiyar Dakile yaduwar cututtuka ta kasa NCDC ta ce sabbin mutane 404 ne suka harbu da cutar Corona a kasar nan a jiya.
Hukumar ta NCDC ta ce an samun bullar cutar ne a jikkunan mutanan da suka fito daga Jihohi 11 na kasar nan ciki harda birnin tarayya Abuja.
NCDC ta ce an salami mutane 15 wanda suka warke daga cutar a cibiyoyin da ake kula dasu.
Haka kuma an samu mutum 1 da cutar ta hallaka a jiya wanda hakan ya kawo adadin mutanen da cutar ta hallaka zuwa dubu 2,985.
Kawo yanzu adadin mutanen da suka harbu da cutar Corona tun bayan bayyanarta a kasar nan sun kai dubu 223,887.