

Ƙarin mutum 75 ne suka harbu da cutar korona a Najeriya ranar Litinin, kamar yadda rahoton hukumar yaƙi da cutuka masu yaɗuwa ta nuna.
Mutanen da suka kamu da cutar sun fito ne daga jiha takwas. Su ne:
- Legas-28
- Akwa Ibom-18
- Ondo-10
- Cross River-9
- Rivers-6
- Edo-2
- Delta-1
- Kano-1
Ya zuwa yanzu, jumillar mutum 254,091 ne suka kamu da cutar, yayin da ta yi ajalin 3,141 tun bayan ɓullarta ƙasar a Fabarairun 2020.