Cutar korona ta sake kama mutum 75 a Najeriya

0 90

Ƙarin mutum 75 ne suka harbu da cutar korona a Najeriya ranar Litinin, kamar yadda rahoton hukumar yaƙi da cutuka masu yaɗuwa ta nuna.

Mutanen da suka kamu da cutar sun fito ne daga jiha takwas. Su ne:

  • Legas-28
  • Akwa Ibom-18
  • Ondo-10
  • Cross River-9
  • Rivers-6
  • Edo-2
  • Delta-1
  • Kano-1

Ya zuwa yanzu, jumillar mutum 254,091 ne suka kamu da cutar, yayin da ta yi ajalin 3,141 tun bayan ɓullarta ƙasar a Fabarairun 2020.

Leave a Reply

%d bloggers like this: