Dan takarar gwamman jihar Jigawa a APC, Hon. Faruk Adamu Aliyu yayi fatali da tsarin sasanto domin gudanar da zaben fidda gwamni

0 89

Dan takarar gwamman jihar Jigawa a tutar Jam’iyyar APC Faruk Adamu Aliyu ya jaddada matsayarsa na tabbatar da gudanar da zaben fidda gwamni dan takarar gwamna a tutar jam’iyyar APC.

Tare da yin fatali da tsarin sasanto.

Faruk Adamu Aliyu ya bayyana hakan ne a yau Juma’a a birnin Dutse a lokacin dayake kaddamar da takararsa a gaban magoya bayansa.

Ya kuma bukaci gwamna Muhammad Badaru Abubaka dayaji tsoron Allah kuma ya zama mai Magana daya.

Kamar yanda a kwanakin baya yace, babu wani dan takarar dayake goyan bayan a cikin masu neman yiwa jam’iyyar Takara a zaben 2023.

Aliyu ya kuma bukaci gwamna Badaru daya amince a gudanar da zaben fidda gwani cikin gaskiya da adalci a tsakanin yan Takarar.

Ya kara da cewa dole ne a tabbatar da gaskiya da adalci a dukkanin zabukan fidda gwani da za’agudanar da fadin jihar nan.

Leave a Reply

%d bloggers like this: