EFCC bata kama tsohon Gwamnan jihar Kano ba, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso

0 119

Jagoran cibiyar sadarwa ta kungiyar Kwankwasiyya, Mallam Sunusi Bature Dawakin Tofa yace hukumar EFCC bata kama tsohon Gwamnan jihar Kano ba, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso kamar yadda ake yadawa a kafafen yada labarai.

Jagoran, cikin wata sanarwa, yace Kwankwaso ne da kansa ya ziyarci ofishin hukumar domin wanke kansa dangane da wasu zarge-zarge marasa tushe da ake tuhumarsa.

Yace tsohon Gwamnan ya ziyarci helkwatar hukumar domin bayar da bayaninsa dangane da zarge-zargen kuma ya gana da jami’an hukumar dake yaki da cin hanci da rashawa na wasu awanni.

Sanarwa ta kara da cewa tsohon ministan tsaron ya bayyana zarge-zargen a matsayin bita da kullin siyasa.

Leave a Reply

%d bloggers like this: